Bello El-rufai Shine Mafi Cancanta Yawakilci Al’ummar Kaduna Ta Arewa – Kwamared Musa Mohammed

Masani a harkar siyasa Kuma mamba a jam’iyar APC a jihar kaduna Kwamared Musa Mohammed ya bayyana nagartar Bello El-Rufai Dan takarar kujerar Majalisar kaduna ta Arewa ta fuskoki da dama wanda yake ganin shi ne mafi cancanta wakilci al’umma.

Yayin da yake tattaunawa da manema labari ranar Alhamis a kaduna game da wanda zai zama jagora kuma wakilin al’ummar kaduna ta Arewa a Majalisar tarayya na gaba a 2023, masanin ya bayyana Bello El-Rufai a matsayin dan takarar da yafi nagarta acikin sauran Yan takaran.

“Bello El-Rufai shi ya cancanci ya zama wakilin al’ummar kaduna ta Arewa a 2023”

Kwamared Musa ya bayyana cancanta, hazaka, Nagarta, sanin yakamata na Malam Bello El-Rufai matsayin muhimman abubuwan da za su sa a zabi shi a matsayin wakilin al’ummar kaduna ta Arewa.

“Ina Kira ga al’ummar kaduna ta Arewa da su zabi MALAM BELLO EL-RUFAI a matsayin dan Majalisar wakilai da zai wakilce mu domin samun wakilci nagari”.

Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started